Добавить новость
ru24.net
World News in Dutch
Октябрь
2016

Jam’iyyun siyasa sun bukaci gyaran tsarin mulki tare da soke wasu hukumomi a jihohi

0

Gamayyar kungiyar jam’iyyun siyasa a yankin kudu maso yammacin Najeriya ta kira majalisun tarayya su yiwa kundun tsarin mulkin kasar gyarar fuska da zai tabbatar da kawar da hukumomin zabe na jihohi.

A taron da suka gudanar domin bayyana rashin jin dadinsu dangane da yadda hukumomin zabe na jihohi ke bayyana jam’iyyun dake mulki a jihohin nasu a matsayin wadanda suka lashe zabukan da ake gudanarwa.

Shugaban jam’iyyar UPN Femi Paida a jihar Ogun yace ko kadan yadda jam’iyyun dake mulki a jihohinsu suke bayyana cewa su ne suka lashe zabuka bai dace ba.

KU KARANTA KUMA: Za’a tafka muhawara ta karshe tsakanin Trump da Hillary

Yayi misali da zabukan da ka gudanar kwanan nan a jihar Ogun inda jam’iyyar APC mai mulki ta lashe zabukan da aka gudanar a kananan hukumomi ishirin na jihar da kuma na yakunan cigaban al’umma talatin da bakwai.

Cikin kansiloli kuwa biyu kacal aka baiwa jam’yyar UPN da PDP mai kujera daya.

Kawar da hukumomin zaben jihohi zai taimaka wurin dorewar dimokradiya a Najeriya.

Otunba Paida yace matakan da ake dauka yanzu domin gudanar da zabuka basu dace ba don haka, majalisun tarayya su zauna su yi gyara a kundun tsarin kasar.

The post Jam’iyyun siyasa sun bukaci gyaran tsarin mulki tare da soke wasu hukumomi a jihohi appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.




Moscow.media
Частные объявления сегодня





Rss.plus
















Музыкальные новости




























Спорт в России и мире

Новости спорта


Новости тенниса